webnovel

ƘWAI A BAKA!

REALSMASHER · Teenager
Zu wenig Bewertungen
1 Chs

THRILLER

💠💠💠💠💠

©®AS-2023.

*♡ƘWAI A BAKA¸.•💥*

(Yᴀ ғɪ ᴋᴀᴢᴀ ᴀ ᴀᴋᴜʀᴋɪ)

Nᴀ

*HAWWA__B__KUMO.*

(Rᴇᴀʟ Sᴍᴀꜱʜᴇʀ).💕

*WATTPAD:REAL-SMASHER.*

*AREWABOOKS:REALSMASHER.*

••••••••••

*Bɪꜱᴍɪʟʟᴀʜɪʀ Rᴀʜᴍᴀɴɪʀ Rᴀʜɪᴍ.*

*It's all about:#Masturbate,#Porn,#Adoption,#Orphan#Fate,#Dad,#Daughter,#NigeriansNiger,#Arrogance,#Hated,#Twist & #Romance..*

*THRILLER*

•••Kallonshi take cike da wani irin yanayi tace "Baby tunda Allah ya bamu namu ɗan,think ya kamata mu mayar da *BAYAH* inda muka ɗaukota,mu mayar da ita Orphanage,dama can ne gidansu,nan ta taso,nan ta sani,ba ta da kowa,mu muka mayar da ita mutum,ba tare da sanin su waye iyayenta ba,ta wace hanya aka sameta,mun ɗaukota mun kawota gidanmu,mun mayar da ita ƴa,mun bata suna me ma'ana,mun mata abubuwa da yawa.. Yanzu lokaci ya yi da zamu mayar da ita,saboda ba da jimawa ba za mu haifi ɗanmu,wanda ni da kai muka samar ta hanyar aure da ƙwaiyayen halittarmu,BAYAH ba ta da gurin zama a nan,she belongs to nowhere bayan orphanage,ka fahimceni dan Allah,bazan iya zama da ita ba,bazan iya sake kallonta a matsayin ƴa ba,bazan iya mata abunda nai mata a baya ba,bazan iya haɗa soyayyar ɗan da zan haifa da wani abu ba,tun kafin ta fuskanci tozarcina ka ɗauketa ka fitar min ita daga gidana.." Cikin faɗa yana mata wani kallon rainin wayo yace "ur house? Wafaa are u crazy? Kina ganin dan kina da ciki hakan zai sa nayi abandoning my daughter? My kid? My little girl BAYAH? Kina ganin kou ƴaƴa nawa na haifa dake zan bar BAYAH ta koma orphanage? A tunaninki zan iya rabuwa da ita? U're wrong Wafaa,bazan taɓa iya rayuwa babu BAYAH ba, she's the source of my life and happiness,a yau da kika ganki ciki duk kin manta da komai da ya faru tsayin shekaru 10,kina min magana na ɗauki yarinyata da nake tsananin so,yarinyar da a dalilinta da addu'o'inta Allah yaji ƙanmu ya azurtamu da samun ƙaruwa,kin manta da abunda kikai alƙawari? Wafaa ina tunaninki? Ina humanity ɗinki yaje? I can't take my daughter back to that house da ake kira orphanage,ita ba gama garin yarinya bane,ba irin yaran da kike zargin sun samu ta banzar hanya bane,yarinyata tsarkakakkiya ce,she's pure,i can't live without her,kin gane?" Hawaye na sauka idon Wafaa tana masa wani kallo kamar a tsorace tace "*ZAHEED!* Ni kake cewa kana son yarinyar da muka raina? Ni kake faɗama baza ka iya rayuwa babu ita ba? Har kake faɗan kou ɗanka na cikinka baza ka iya haɗa soyayyarsa da ita ba? Wow! This sounds good.. ZAHEED da wannan soyayyar da kake ma yarinyar nan me zai hana baza ka aureta ba? Ƙarewar so ka mayar da ita kishiyata,ka aureta ta zama matarka,ka raba mana kwana ni da ita,ka shiga ɗakinta kai mata irin abunda kake min,shi ne zan san da gaske ka damu da ita,shi ne zan tabbatar ba ka son tai nisa da kai.. Da na san ɗauko shegiyar yarinyar nan zai iya zame min masifa a rayuwarta,wallahi bazan taɓa bin hanyar Nassarawa ba bare har na ganta ta bani tausayi,shegiyar yarinya mara asali,mara gata,wanda iyayen da suka haifeta suka jefar,suka wofintar.. Ashe annoba ce ita,dole kowa yaƙi ɗaukanta sai mu da..." Kafin ta sake furta wani abu taji tau² ya ɗauketa da tagwayen marukan da suka sa tai shiru,wani irin kallonta yake zuciyarsa na tafarfasa kamar za ta fito daga ƙirjinsa,maganganunta sosai sukai tasiri a zuciyarsa,cikin kaushin murya yana nunata tare da zazzaro mata duka girman idanunsa da suka kaɗa sukai jaa yace "don't dare call her da waɗannan dirty sunayen.. My daughter is pure,ke kika jahilci kanki Wafaa,yarinyata kou ke baza ki nuna mata asali ba saboda ni ne mahaifinta,and zan iya zame mata komai,zan iya zama uwa kuma uban at the same time,tunda a yau saboda ganinki da ciki ya sa kinyi breaking promises,idan baza ki iya zama da ita ba the doors are open,za ki iya barin gidan nan duk lokacin da kika so,Bayah ta zo kenan,idan kinga ta bar gidan nan,sai dai in aurar da ita nayi kou kuma mutuwa tayi,wannan abu biyun su kaɗai za su iya rabani da ƴata,kisa wannan a ranki.." Daga haka gudun zuciya kada ya ɗebeshi yai abunda ba dai² ba,da sauri cike da wani irin ƙunar zuciya ya juya ya bar mata ɗakin..

*

Tsaye take bakin staircase ta rufe baby face ɗinta tana kuka me cike da ban tausayi,duk maganganun nan akan kunnenta suke sauka ɗaya bayan ɗaya,tunda ta taso bata taɓa sanin cewa ita marainiya ce wanda akai adopting from orphanage ba sai yau,she thought yanda Mom da Dad suke bala'in sonta,basa son ganin damuwa akan fuskarta su ne iyayenta,su suka haifeta,a school da sunan Dad take amfani,idan an tambayeta her mother's name za tai saurin cewa Wafaa Da'wud,ashe duk basu suka haifeta ba? Suma ɗaukota sukai daga orphanage? Ita marainiya ce wanda bata da kowa? Da gudun bala'i ta ƙarasa hawa benen ta wuce ta buɗe ƙofar bedroom ɗinta,saman gado ta faɗa ta fasa wani irin gigitaccen ƙara tana tattaƙure kanta tana kallon ɗakin da komai na ciki kamar tana jin tsoronsu,idan akace mata wata rana za tazo da taji ta tsani komai da kowa except for Dad da har yanzu zuciyarta ke tsananin so za ta ƙaryata,idan wani yace wata rana Mom za ta ƙita har taji asalin wace ce ita a bakinta da wuri za ta ƙaryata,sai gashi yau ta ji maganganu mabanbanta daga bakunan mutanen da baza su taɓa mata ƙarya ba,mutanen da ta ɗauka su ne duniyarta,su ne rayuwarta da komai nata,tambayar farko data fara yiwa kanta shin ina iyayenta? Me yasa suka jefar da ita? Me tai musu da suka banzatar da rayuwarta ta taso a orphanage? Ina ne gidansu? A wace duniya iyayenta suke? Shin suna sane suka barta tsayin lokacin nan? Kou kuwa maganar Mom Wafaa ne ita annoba ce? Shi yasa basa sonta? Shi yasa suka kasa riƙeta? Shi yasa suka yar da ita tun tana yarinya?

*

Buɗe entrance da akayi yasa Wafaa ɗago face ɗinta da yai kaca² da hawaye,tashin hankali ƙarara cikin idanunta,damuwa me girma kwance a fuskarta,Zaheed dake tsaye doorway shi bai ƙarasa shigowa ba kuma bai yi magana ba,ganin yanda take kuka tana kallonsa irin kallon nan dake bayyana rashin gaskiya,tsoro me girma kwance cikin idanunta,jikinsa a matuƙar mace zuciyarsa na bugawa fast² ya ɗaga ƙafarshi yana shigowa yana kuma kallonta,irin kallon nan me cike da tuhuma,kallo me razanarwa me firgitar da mutum,tun kafin yayi magana ta gama tsurewa cikinta banda hautsinawa babu abunda yake tana jin kamar za ta saki fitsari a gurin saboda tashin hankali,sai kakkare bayanta take tana girgiza masa kai bakinta na ɓari,yanda yake kallonta haka itama take kallonsa tana son tai magana amma tana tsoron abunda zai biyo baya,Zaheed dake ci gaba da nufarta ya juya yana kallon cikin parlon,lokaci ɗaya ya hau ƙwala kiran "Bayah! Girl!! Baby!!!" Da wani breaking voice Wafaa ta furta "i'm so sorry Babe.. Wallahi it was not intentional.. Ban san haka zai faru ba,ban daketa da wani manufa ba,sai saboda ta min taurin kai" zazzaro idanu Zaheed yayi yace "what do u mean Wafaa? This small girl? Ita kika doka? Duka da bulala? Where's she? Me ya samu yarinyata!?" Yai mata tsawar da sai da ƴaƴan cikinta suka wani irin juya,ganin ya nufota kamar mayunwacin zaki,da gudun bala'i ta kauce saboda masifaffen tsoron daya shigeta,idanunsa sai karaf akan Bayah dake yashe ƙasa,a tsorace ya ƙarasa inda take yana sake zazzaro idanuwa cikin kaɗuwa yace "Wafaa did u killed my daughter?" Cikin ɓarin jiki da murya tace "ban mata komai ba,dukanta kawai nayi" cikin tsawa yace "u killed her! Idan baki kasheta ba me yasa take a haka? Me yasa zan ganta kwance under floor? Baby! Wake up.. Open ur eyes,here is ur Dad,i'm here for u girl,babu abunda zai sameki,ok!?" Cikin kuka Wafaa tace "Zaheed! I'm sorry" cikin ihu ya hantareta "sorry for ur self Wafaa! I regret everything about u,from the beginning up to now,kisan kai? Are u this wicked? Tsanar da kikewa Bayah har ya isa yasa ki iya kasheta?" Hawaye suna sauka idanunsa masu zafi yace "i never know haka kike,wallahi da ban aureki ba,da ban yarda na haɗa wani alaƙa dake ba,i so so so regret of knowing u,na yi nadamar shigowarki rayuwata.. I hate u Wafaa! And I really do.. Idan wani abu ya samu this innocent girl wallahi bazan barki ba,ba zan taɓa yafe miki ba" hannu ta kai za ta dafa shoulder ɗinsa da ƙarfi ya turata cikin ihu yace "don't dare touch me.. Ke azzaluma ce,muguwa me son kanta,na yi nadamar saninki.." Ƙarar data kwaɗa yasa shi juyawa yana kallonta duk da bai so ya kalleta ba,yashe a ƙasa ya ganta ta faɗa kan cikinta sai murƙususu take,tana faɗin "wayyooo cikina.. Zaheed help me kada na rasa cikina.. Take me to the hospital Zaheed kada na rasa Babynah.."

```#Wai³! Bala'i akan masifa,da gaske Bayah ta mutu? Me zai faru da cikin jikin Wafaa? Shin wa ya kamata Zaheed ya fara cetowa? Rayuwar waye yafi muhimmanci a gurinsa Bayah kou Wafaa? The battle it's between a daughter and a wife! Don't missed out.. For group request chat me up https://wa.me/+2348165726609````

#Follow

#Comment

#Vote

#Share

#WATTPAD:@REAL-SMASHER

#AREWABOOKS:@REALSMASHER

#THREAD:@ASLISMASHER

#ASLI-SMASHER.